1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Libiya: Masunta sun gano gawarwaki a Teku

Abdul-raheem Hassan
April 18, 2017

Wasu masunta a Libiya sun gano gawarwaki 28 a cikin teku kusa birnin Sabratha. Hukumomi a kasar sun ce mutanen sun mutu ne sakamakon rashin ruwan sha da abinci gabannin nutsewarsa.

https://p.dw.com/p/2bRsw
Libyen Tote Flüchtlinge an der Küste nahe Zawiya
Hoto: picture alliance/AP Photo/IFRC/M. Karima

Kwamandan kula da tsaron sashin cikin gida a Libiya Ahmaida Khalifa Amsalam ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Reuters cewa an binne gawarwakin da masuntan suka gano cikin ruwa a rami guda ciki kuwa har da mata hudu.

A tun bayan juyin juya halin da ya kifar da mulkin tsohon shugaban Libiya Muammar Gaddafi a shekara ta 2011, kasar ta zamo kofa ga bakin haure sama da dubu 150 a duk shekara suna silalewa ta ruwa zuwa nahiyar Turai.