1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Likitocin Rasha biyu sun halaka a Aleppo

Gazali Abdou Tasawa
December 5, 2016

Amirka da Rasha na shirin tattauna batun ficewar illahirin 'yan tawaye daga birnin Aleppo

https://p.dw.com/p/2Tn5d
Syrien Zerstörter Operationssaal in Atareb westlich von Aleppo
Hoto: Reuters/Social Media

A kasar Siriya wasu jami'an kiwon lafiya biyu 'yan kasar Rasha da suka hada da mace daya sun halaka a yayin da wani na uku ya ji munmunan rauni a cikin wasu hare-haren roka da 'yan tawaye suka kaddamar kan wani gidan assibiti na wani kauyen da ke kusa da birnin Aleppo. 

Wannan hari ya zo ne a daidai lokacin da kasashen Rasha da Amirka ke shirin soma wata tattaunawa a wannan mako kan batun ficewar illahirin 'yan tawaye daga birnin Aleppo wanda a halin yanzu dakaran gwamnatin Siriyar suka kwace sama da kashi biyu daga cikin uku na unguwannin da ke a karakshin ikon 'yan tawayen.

 Sai dai mayakan 'yan tawayen sun yi watsi da wannan tayi na ficewa daga birnin na biyu mafi girma a kasar ta Iraki tare da  shan alwashin ci gaba da yaki har sai sun ga abin da ya ture wa buzu nadi.