1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Lokacin mulkin mata yazo a Nahiyar Africa..

January 17, 2006
https://p.dw.com/p/BvBw
Annan ya kai ziyara asibitin yara a Nijer
Annan ya kai ziyara asibitin yara a NijerHoto: AP

Zambia......................

Shugabar adawa a kasar Zambia, wato Edith Nawakwi, tace da alama zata iya zamowa mace ta biyu da zata jagoranci wata kasa a nahiyar Africa.

A cewar Edith Nawakwi, hakan ya samo asali ne bisa kwarin giwa data dada samu a sakamakon rantsar da Ellen Jonhson Sirlef da akayi jiya, a matsayin shugabar kasar Liberia, wacce ta kasance mace ta farko da zata jagoranci shugabancin wata kasa a nahiyar Africa.

Edith Nawakwi yar shekaru 45, data taba rike mukamin ministar kudi ta kasar Zambia, a lokacin mulkin shugaba Chiluba, ta tabbatar da cewa lokaci yayi da mata zasu zage damtse a nahiyar Africa, wajen ganin ana damawa dasu yadda yakamata a harkokin mulki na kasashen su.

A cewar shugabar adawar ta jam´iyyar FDD,babban burin ta idan ta zamo shugabar kasar ta Zambia, shine inganta tattalin arziki, don kyautata rayuzwar talakawan kasar.