1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Louise Arbour ta soki Iran da taka yancin mata

March 6, 2007
https://p.dw.com/p/BuQK

A yayin da ya rage kwanaki ƙalilan a gudanar da bikin ranar dunia, ta yaya mata, komishinar kulla da kare haƙƙoƙin jama´a ta MDD, Louise Arbour, da kiri taron manema labarai a birnin Geneva, na ƙasar Suizland.

Jami´ar, ta bayyana takaici, a game da yadda wasu ƙasashe, ke ci gaba da cin zarafin yaya mata.

Ta bada misali da Iran, inda a cewar ta, ranar lahadin da ta wuce, hukumomi su ka yi awan gaba, da mata fiye da 30, a lokacin da su ka shirya wata zanga-zangar lumana, gaban kotun musulunci ta ƙasa, domin neman belin wasu dangi su mata, guda 5, da halin ke cikin kurkuku.

Gwamnati na tsare da su tun ranar 8 ga watan Maris na sheakara da ta gabata.

Matan da a ka capke ranar lahadi sun shiga yajin ƙin cin abinci.

Komishina Arbour ta yi kira ga hukumomin Teheran su gaggauta sakin wannan mata.