1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

M.Abbas ya rusa gwamnatin haɗin kan Palestinu, tare da kafa dokar ta ɓace

June 14, 2007
https://p.dw.com/p/BuIq

A ɗazunan Shugaban hukumar Palestinawa Mahamud Abbas, ya sa hannu a kann dokar rusa gwamnatin haɗin kann ƙasa, tare da dokar ta ɓace a fadin ƙasar baki ɗaya.

Kazalika shugaban hukumar Palestinawa ya ambata shirya saban zaɓe, da zaran al´ammura sun daidaita.

Mahamud Abbas ya dauki wannan mataki, a matsayin martani ga tashe-tashen hankullan da ke wakana tsakanin ƙungyiyoyin Fatah da na Hamas.

A yammacin yau dakarun Hamas, sun bayyana fille kann wani jigo a ƙungiyar fatah, kazalika sun yi kaca-kaca, da gidan rediwan muryar Palestinu.

Rikici tsakanin ɓangarorin 2 a yau alhamis ya hadasa mutuwar mutane kimanin 20.

A halin da ke ciki, ƙasashe da ƙungiyoyi daban-daban na dunia, na ci gaba da yin Allah wadai da wannan tashe-tashen hankulla.

Masu kulla da harakokin da ke gudana a gabas ta tsakiya, sun danganta rusa gwamnatin Palestinu, a matsayin da zai ida dagula zaman lahia a wannan yanki.