1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macron zai kawo sauyi a Tarayyar Turai

May 14, 2017

Emmanuel Macron da ya sha rantsuwar kasancewa shugaban Faransa mafi kankancin shekaru, ya yi alkawarin kawo sauyi a kungiyar Tarayyar Turai.

https://p.dw.com/p/2cwYS
Frankreich Paris Amtseinführung Emmanuel Macron
Hoto: Reuters/C. Hartmann

Anasarn Macron zai tabbatar da goyon bayansa ba wai ga kungiyar ta EU kadai ba, har ma da Tarayyar Jamus, a lokacin ganawarsa da shugabar gwamnati Angela Merkel a ziyarar farko da zai kawo Berlin a gobe.

Kazalika a wannan Litinin din ce ake saran mai shekaru 39 da haihuwar, kuma tsohon ministan tattalin na Faransa, zai gabatar da sunan fraiministansa, a cewar majiya mai tushe da ke kusa da fadar shugaban kasar.

Kafofin yada labarun Faransan dai sun ruwaito rade-radin yiwuwar nada magajin garin Le Havre mai ra'ayin mazan jiya Edouard Philippe a matsayin sabon fraiministan, sai dai zaben 'yan majalisar wakilai da zai gudana a wata mai zuwa zai iya sauya komai, tunda wajibi ne jam'iyyar da ta fi rinjayen kujeru ta kasance mai kafa gwamnati.