1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce Iraqi na ta ƙara faɗawa cikin ruɗami da tashe-tashen hankulla.

November 23, 2006
https://p.dw.com/p/Buaf

Bisa wani rahoton baya bayan nan da Majalisar Ɗinkin Duniya ta buga, a cikin watan Oktoba da ya gabata kawai, mutane, a galibi fararen hula, fiye da dubu 3 da ɗari 7 ne suka rasa rayukansu a tashe-tashen hankullan da ke ta ƙara haɓaka kamar wutar daji a Iraqi. Ba a dai taɓa samun irin wannan adadin a cikin wata ɗaya kawai ba kawo yanzu. Hare-hare da kashe-kashen da ake ta yi a ƙasar ya sa ɗimbin yawan jama’a na tashi daga matsugunansu, wasu ma na yin ƙaura zuwa ƙasashen ƙetare da ke maƙwabtaka da Iraqin. Majalisar sinkin Duniyar dai ta ƙiyasci cewa, a ko wane wata kusan ’yan ƙasar Iraqin dubu 100 ne ke neman mafaka a Siriya ko kuma Jordan. Gaba ɗaya kuma, tun da aka fara yakin Iraqin, mutane kimanin mmiliyan ɗaya da digo 6 ne suka fice daga ƙasar, inji rahoton.

Game da halin da ake ciki yanzu dai, shugaban Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya a Iraqin, Gianni Magazzeni, ya bayyana cewa:-

„Tsarin tashe-tashen hankullan ya sake a cikin ’yan watannin da suka wuce. A nawa ganin, mun sami ƙarin tashe-tashen hankulla tsakanin mabiya ɗariƙu ko kuma na ƙabilanci. Ban da haka, akwai kuma hare-haren da aka kai, waɗanda ba ’yan yaƙin gwagwarmaya da ’yan ta’adda kawai ne ke da hannu a cikinsu ba, har da ma gungun ’yan bindiga da kuma na masu aikata miyagun laifuffuka.“