1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Birtaniya tana tattauna farmaki a Siriya

Suleiman BabayoDecember 2, 2015

Majalisar dokokin Birtaniya tana mahawara mai zafi kan shirin neman kaddamar da farmaki kan tsagerun kungiyar IS a Siriya.

https://p.dw.com/p/1HFyK
Großbritannien Rede Cameron zur IS Bekämpfung im Parlament
Hoto: picture alliance/empics

Majalisar dokokin Birtaniya tana tattaunawa a wannan Laraba kan shirin shiga kai hare-hare sansanonin tsagerun kungiyar IS da ke cikin kasar Siriya. Firaminista David Cameron ya kara kaimi kan shirin tun bayan hare-haren da aka kai birnin Paris na kasar Faransa da kimanin mutane 130 suka hallaka cikin watan jiya na Nuwamba.

Majalisar dokokin za ta shafe sa'oi tana tattauna duba yuwuwar kaddamar da hare-haren. Shugaban marasa rinjaye na majalisar Jeremy Corbyn kana shugaban jam'iyyar adawa ta Labour ya bukaci kar a yi gaggawa wajen shiga yakin. Ana fafata mahawara mai zafi a majalisar dokokin ta Birtaniya kan wannan shiri.