1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Dinki Dunia ta maida wa gwamnatin Erythrea martani

December 8, 2005
https://p.dw.com/p/BvHV

Majalisar Dinkin Dunia ta maida martani ga wa´adin kwanaki 10, da gwamnatin Erythrea ya baiwa wasu daga jami´an ta, na su fita daga kasar.

Wannan umurni ya shafi jami´an soja, da kuma na fara hulla dake zaune a Asmara babban birnin kasar ,domin sa iddo a kannyarjejeniyar zaman lahia ,da aka cimma, tsakanin Erythrea da Ethiopia, a shekara ta 2000, bayan sun share shekaru 2 su na gwabzawa.

Kakakin sakatare Jannar na Majalisar Dinki Dunia, ya hurta cewa ko da mafarki, wannan jami´ai ba za su fita ba daga Erythrea, ya kuma yi kira ga gwamnati, da ta janye wannan umurni cikin gaggawa.