1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Dinkin Duniya za ta yi watsi da matakin Amirka

Abdourahamane Hassane
December 17, 2017

Kwamitin sulhu na MDD na yin nazari a kan wani kudiri wanda zai yi watsi da matakin da shugaba Donald Trump ya dauka a kan birnin Kudus.

https://p.dw.com/p/2pV6a
Israel verschärfte Sicherheitsvorkehrungen am Tempelberg in Jerusalem
Hoto: Getty Images/AFP/T. Coex

Kasar Masar  ita ce ta gabatar da wannan kudiri wanda zai yi fatali da matakin na Amirka. Daftarin kudirin wanda manbobi 14 na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniyar suka amince da shi ya tanadi kushe ikirarn da shugaban na Amirka ya yi tare da hanashi yin tassiri.