1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Dinkin Duniya zata rage yawan taimakon abinci a Sudan

April 29, 2006
https://p.dw.com/p/Bv0J

Karancin kudaden taimako daga kasashe masu ba da agaji, ya sa a dole MDD ta rage yawan taimakon kayan abinci da take bawa al´umar kasar Sudan dake cikin halin ni ´ya su. Wata mai magana da kungiyar samar da abinci ta MDD ta ce daga mako mai zuwa za´a rage kashi 50 cikin 100 na yawan abincin da ake ba mutane kimanin miliyan 6.1 a kowace rana. Jami´ar ta ce daukar wannan matakin ya zama dole don ba su da wani zabi. Daga cikin wadanda wannan matakin ya shafa akwai mutane miliyan 3 na lardin Darfur dake yammacin Sudan.