1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar dokokin Jamus za ta yi muhawara

Abdourahamane HassaneSeptember 7, 2016

Majalisar dokokin ta Jamus watau Bundestag za ta tattauna batun kasafin kudin kasar na shekara ta 2017.

https://p.dw.com/p/1Jwr6
Deutschland Bundestag Armenienresolution Abstimmung
Hoto: Getty Images/AFP/S. Gallup

An shirya shugabar gwamnatin ta Jamus Angela Merkel za ta yi jawabi a lokacin bude taron.Wanda ya zo kwanaki biyu kacal bayan mummunar kayan da jam'iyyar da ke yin mulki watau CDU ta sha a zaben jihohin da aka yi ran Lahadin da ta gabata a jihar Mecklemburg-Vorpommern.

Masu aiko da rahotnnin sun ce da alama za a tafka muhawara mai zafi a lokaci zaman taron da za a kwashe kwanaki hudu ana tattauna sabon kasafin kudin kasar.