1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Makokin tunawa da harbo jirgin Malesiya

Gazali Abdou Tasawa
July 17, 2017

A kasar Ukraine a wannan Litinin ce dangi da 'yan uwa da aminnan arzikin mutanen da suka mutu a cikin jirgin saman Malaisian Airlines da aka harbo da makami mai lizzami a gabashin kasar lokacin yaki ke zaman makoki.

https://p.dw.com/p/2gdiu
Australien | Angehörige gedenken den Absturzopfer von Malaysia-Airlines-Flug MH17
Hoto: Reuters/D. Gray

A lokacin wannan taron makoki wanda zai gudana a wannan Litinin a karkashin jagorancin sarki William Alexander da Sarauniya Maxima na masarautar Hollande, Mutane kimanin 2000 daga cikin dangin mamatan za su yi zobe a wani shingen itatuwa 298 da aka shuka a wurin da jirgin ya fado a matsayin shaidar nuna alhini ga mutanen 298 da suka rasu a lokacin faduwar jirgin. 

A ranar 17 ga watan Yulin shekara ta 2014 ne dai a tsakiyar yakin kasar Ukraine wani makami mai lizzami kirar kasar Rasha ya kakkabo  jirgin na Malesiya Airlines dauke da fasinjoji 298 da suka hada da 'yan kasar Hollande 196.