1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Malamai sun bijire wa jami'o'in isra'ila

Gazali Abdou tasawaOctober 27, 2015

Wasu malamai kimanin 340 da ke koyarwa a jami'o'i kimanin 70 na Isra'ila sun dakatar da aiki domin nuna adawarsu da take hakkin Palasdinawa da Isra'ila ke yi

https://p.dw.com/p/1Guvx
Tel Aviv Universität, Israel
Hoto: Dyan Andriana Kostermans

Wasu kwararrun malaman jami'a kimanin 340 masu koyarwa a jami'o'i sama da 70 na kasar isra'ila sun bada sanarwar shirin raba gari da jami'o'in kasar ta Isra'ila dama kaurace wa duk wasu tarurrukan da jami'o'in za su shirya ko za su dauki dawainiyar shiryasu a nan gaba.

Malaman wadanda suka bayyana wannan matsayi nasu a cikin wata budaddiyar wasika da suka wallafa a wannan Talata a cikin jaridar The Guardian mai fita kullun sun ce sun yi haka ne domin nuna rashin amincewarsu da abin da suka kira yawaitar take hakin dan Adam da Isra'ilar ke yi wa daukacin al'ummar Palasdinawa.

Daga cikin masanan da suka bada goyan bayansu ga shirin raba gari da jami'o'in kasar ta Isra'ila wasunsu sun fito daga wasu fitattun jami'o'in Birtaniya kamar su Oxford da Cambridje.