1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Malesiya na takun saka da Koriya ta Arewa

Abdul-raheem Hassan
March 7, 2017

Jami'an tsaron kasar Malesiya sun killace ofishin jakadancin Koriya ta Arewa da ke Kuala Lampur da nufin gudanar da bincike kan wasu jami'ai da ake zargi da kashe dan uwan shugaba Kin Jong-un.

https://p.dw.com/p/2YkM6
Malaysia Botschaft Nordkoreas in Kuala Lumpur | Protest
Hoto: Reuters/A. Perawongmetha

Ma'aikatar cikin gidan kasar Malesiya ce ta bayyana daukar wannan mataki da nufin tantance wasu jami'an da ake zargi da hannu wajen kisan dan uwan shugaban Koriya ta Arewar. To sai dai wannan zazzafar mataki na zuwa ne adai-adai lokacin da rahotanni ke tabbatar da hukuncin da Koriya ta Arewa ta ayyana, na haramta wa 'yan Malesiya mazauna Koriya ta Arewa ficewa da ga kasar a wannan Talata. Wannan dai na zuwa ne a wani batu da ake ganin ya kai kololuwar tsamin dangantaka tsakanin kasashen biyu a kan zargin kashe dan uwan shugaban kasar Koriya ta Arewar.