1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Manyan kasashe biyar na MDD za su yi taro domin daukar matsayi guda akan kasar Iran

January 26, 2006
https://p.dw.com/p/BvAp

Ministocin kasashe dake da wakilcin dundundun a majalisar dinkin duniya, a mako mai zuwa idan Allah ya kai mu zasu gudanar da taro a birnin London domin shawarta matakin da zasu dauka na gaba a game da takadamar Nukiliyar kasar Iran da yaki ci yaki cinyewa.

Wani jamiín harkokin waje na kasar Britaniya wanda ya bukaci kada a baiyana sunan sa, yace ministocin kasashen biyar dake kujerar dundundun a majalisar dinkin duniya wadanda suka hada da Britaniya da Faransa da Rasha da China da kuma Amurka bugu da kari tare da kasar Jamus zasu tattauna a daura da taron gidauniya domin tallafawa kasar Afgahnistan don yanke shawarar da ta dace a game da takadamar Nukiliyar ta kasar Iran .