1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mari le Pen za ta fuskanci shari'a

March 2, 2017

Majalisar dokokin Kungiyar tarrayar Turai ta amince da cire rigar kariya ta jagorara jam'iyyar masu kyamar baki Mari Le pen ta Faransa.

https://p.dw.com/p/2YWsD
Frankreich - Marie Le Pen im Europaparlament
Hoto: picture-alliance/AP Photo/J. F. Badias

Kotu a kasar Faransa ita  ta bukaci majalisar da ta cire rigar kariyar 'yar siyasar sakamakon yadda ta ce an sameta da laifin watsa wasu bidiyo na kisan jama'ar da 'yan Kungiyar IS suke yi a shafinta na Twitter a shekarar bara.A cikin watan Afrilu na shekara ta 2016 wani alkalin mai gudanar da bincike ya gayaceta domin ya saureta a kan wannan batu amma ta ki ammsa kira kan cewar tana da rigar kariya.