1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Martani dangane da fara tattaunawar sulhunta gabas ta tsakiya

September 3, 2010

Ƙungiyar Hamas ta lashi takobin cigaba da kaiwa Izraela hari

https://p.dw.com/p/P3x4
Hoto: AP

Ƙungiyar Hamas dake rike da madafan ikon zirin Gaza a yankin Paslastiwa tayi ikirarin cigaba da kai hari akan Izraela, a martanin ta dangane da tattaunawar sulhu da aka kaddamar. Kakakin ƙungiyar Hamas Abu Obeida ya shaidar da cewar Hamas ta haɗe da wasu ƙungiyoyin sa kai 13, domin tsara kaiwa Izraela hare-hare. Bayanan Jaridun ƙasashen larabawa dai na nuni da cewar, babu wani tasiri da tattaunwara zata yi, domin babu yarjejeniyar da za a iya cimma wa ba tare da ƙungiyar Hamas da Irana ba, kasar da ake zargin tana marawa ƙungiyar baya. Shugaba Mahmoud Abbas na Fatah dai shine ke wakiltar Palastinawa a wajen tattaunawar.

Mawallafiya: Zainab Mohammad Abubakar

Edita           : Umaru Aliyu