1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar: Wasu ministoci biyu sun ketare rijaya da baya

Abdourahamane Hassane
December 20, 2017

Sojojin kasar Masar sun kashe wasu mayakan kungiyar IS guda biyar wadanda suka kai hari a kusa da  filin saukar jiragen sama na Al-Arich da ke a arewacin yankin Sinai.

https://p.dw.com/p/2pjOS
Anschlag Ägypten Sinai
Hoto: AFP/Getty Images/M. El Shahed

 

Kungiyar ta IS ta ce ta kai harIn ne da nufin kashe ministocin tsaro da na cikin gida na Masar da suka kai ziyara a yankin domin duba yadda harkokin tsaro ke tafiya. Rundunar sojojin ta Masar ta ce babu ko daya daga cikin ministocin da ya samu rauni, sai dai ta ce hafsoshin soji na gwamnati guda biyu sun mutu a sakamakon harbi wani makamin roka.