1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masu tonon zinariya sun mutu a Burkina Faso

Salissou Boukari MNA
August 28, 2017

Mutane takwas suka mutu yayin da wasu suka samu raunuka, bayan da wani wurin da ake hakar zinariya na gargajiya ya rufta a karamar hukumar Gogo da ke tsakiyar kasar Burkina Faso.

https://p.dw.com/p/2iw80
Kinderarbeit in Goldminen in Burkina Faso
Yara masu tonon Zinare a Burkina FasoHoto: DW

Magajin garin wannan karamar hukuma ta Gogo, Bernard Bouda, ya sanar da wannan labari bayan ziyarar da ya kai a inda hadarin ya afku. Ana sa ran ruwan sama kamar da bakin kwarya da ke zuba a yankunan ne suka haddasa zaftarewar kasa, wanda hakan ta sanya wurin hakar ma'adinan na zinariyar ya fada wa masu aikin tonon ta. Magajin garin na Gogo ya ce bayan hukumomi su tabbatar da mutuwar mutanen, an yi musu jana'iza a garin da wannan hadarin ya afku.

Masu tonon zinariyan na Burkina Faso dai na yin wannan aiki ne duk kuwa da haramcin da hukumomi suka yi ta sabili da lokaci ne na damina inda kasa ka iya zaftarewa a kowane lokaci.