1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin shawo kan matsalar bakin haure a nahiyar Turai

Lateefa Mustapha Ja'afarAugust 21, 2015

Kasashen Birtaniya da Faransa sun bayyana aniyarsu ta kara tsaurara matakan tsaro a kan iyakokinsu domin yaki da matsalar safarar mutane.

https://p.dw.com/p/1GJPX
Matsalar bakin haure a Turai
Hoto: Reuters/P. Rossignol

Kasashen dai sun amince da kafa sabuwar rundunar 'yan sanda ta hadin gwiwa domin dakile ayyukan masu safarar mutane da ke amfani da mashigar karkashin ruwa da ta hada kasashen biyu. Haka kuma sun kafa wani asusun hadin gwiwa na kudi kimanin Euro miliyan 10 a wani sabon yunkuri na kasar Birtaniya domin taimakawa masu neman mafaka da kuma mayar da wasunsu kasashensu na asali.

Rahotanni sun nunar da cewa sakatariyar harkokin cikin gida ta Birtaniya Theresa May da takwaranta ministan harkokin cikin gida na Faransa Bernard Cazeneuve ne suka bayyana sababbin matakan tsaron da suka dauka yayin ziyarar da suka kai mashigar karkashin ruwan da ta hada kasashen biyu a wannan Alhamis.