1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsalar yaduwar masassarar tsuntsaye a Turkiya

January 8, 2006
https://p.dw.com/p/BvDF

Hukumomin Turkiya sun ce matsananciyar murar tsuntsaye na ci-gaba da yaduwa a cikin kasar, bayan an gano cutar a cikin wasu matattun kaji a jihohi biyu dake arewa maso yammacin kasar. Hakan dai ta zo ne bayan rahotannin da aka bayar cewa a karo na 4 dan Adam ya kamu da kwayoyin cutar a wani kauye dake gabashin Turkiya. To sai dai ba´a sani ba ko mutumin wanda shi ne na hudu da ya harbu da kwayoin cutar na dauke da nau´in H5N1, wanda yayi sanadiyar mutuwar wasu yara biyu ´yan´uwan juna a wani asibiti a makon jiya. Sakamakon binciken da aka gudanar akan wata yarinya da ita ma ta rasu bai tabbatar da nau´in kwayoyin na H5N1 ba. Wannan dai shi ne karon farko da ´yan Adam suka rasu sakamakon murar tsuntsayen a wajen nahiyar Asiya, inda akalla mutane 70 suka rasu sakamakon kamuwa da cutar tun bullar ta a shekara ta 2003.