1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MayaƘan taliban sun kashe sojan Britania ɗaya.

August 27, 2006
https://p.dw.com/p/BulR

Mayakan Taliban sun sake kashe soja ɗaya ɗan ƙasar Britania, a wani saban hari da su ka kai yau, a kudancin ƙasar Afghanistan.

Kakakin ministan tsaro a birnin London ,ya ce harin ya wakana, a yammacin jihar Helmand.

Tun ƙarshen watan juli da ya gabata, rundunar tsaro ta NATO, ta karɓi jagorancin sojojin ƙawance a Afgahinstan, a yaƙin da su ke, na kakkaɓe yan taliban.

Daga wannan lokaci, ya zuwa yanzu, ƙungiyar NATO, ta yi assara sojoji 6.

A halin yanzu,Ƙasar Afghanistan, na fuskantar tashe tashen hankulla mafi muni, tun bayan kiffar da yan taliban a shekara ta 2001.