1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Laifina ne faduwar jam'iyyar CDU Inji Merkel

Abdullahi Tanko BalaSeptember 19, 2016

Na ji takaicin faduwar jam'iyyarmu ta CDU a zaben majalisar yankin Berlin inji Merkel

https://p.dw.com/p/1K4wZ
Deutschland Bundeskanzlerin Angela Merkel in Berlin
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Kappeler

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce ta dauki alhakin mummunan kayen da jam'iyyarta ta CDU ta sha a zaben majalisar dokoki a Berlin. Sai dai kuma ta dage cewa ba za ta sauya manufarta kan yan gudun hijira ba.

Merkel ta ce sakamakon zaben da aka yi a karshen mako abu ne mai matukar takaici da rashin jin dadi ga Jam'iyyar CDU.

Ta ce dalilin hakan kuwa shine ba'a yi cikakken bayani da jama'a za su fahimta game da manufarta ta karbar yan gudun hijira ba.

Merkel ta yi alkawarin cewar za ta yi bakin kokari na magance damuwar jama'a akan manufofinta kan yan gudun hijira.