1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ministan tsaro Jamus ya yi kira a rage yawan sojojin kasar a ketare

September 1, 2007
https://p.dw.com/p/BuCc
Ministan tsaron Jamus Franz Josef Jung ya bawa majalisar ministocin Jamus shawarar rage yawan dakarun kasar da ke aikin yaki da ta´addanci a ketare. Jaridar Welt am Sontag ta rawaito ministan na cewa kamata yayi a rage yawan dakarun da sojoji 400 wato izuwa dubu 1 da 400. Ta haka ministan wanda dan jam´iyar CDU ne zai saukaka shawo kan jam´iyar SPD don ta amince da wani sabon tsari na aikin rundunar wadda ake kai ruwa rana kanta. Wannan tsari ya tanadi tura sojojin kundunbala 100 zuwa Afghanistan tare da ba da jiragen ruwan yakin kasar ga aikin yaki da ta´addanci a yankin Kahon Afirka da kuma gabashin Tekun Bahar Rum.