1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ministan tsaron Jamus na kan hanyarsa zua Kwango.

July 2, 2006
https://p.dw.com/p/Burs

Minstan tsaron Jamus, Franz-Josef Jung, ya tashi yau daga birnin Berlin don kai ziyara a ƙasashen Jumhuriyar Dimukraɗiyya ta Kwango da kuma Gabon. Wannan ziyarar dai na dangane ne da girke dakarun Jamus da za a yi a ƙasashen biyu, ƙarƙashin laimar rundunar kare zaman lafiyar da Ƙungiyar Haɗin Kan Turai za ta tura a Kwangon, don tabbatad da tsaro a loakcin zaɓen ƙasar, wanda za a gudanar a ƙarshen wannan watan.

Ministan ya faɗa wa maneman labarai cewa, sojojin za su dawo gida kafin kirismeti. A ziyara tasa dai, Franz-Josef Jung, zai yi rangadin wasu sansanonin soji ne a biranen Kinshasa da kuma Libreville, sa’annan kuma ya tattauna batutuwan da suka shafi harkokin siyasa da shugabannin yankin. A nan Jamus dai, an yi ta muhawara mai tsanani kan girke dakarun a Kwango, saboda ganin hakan da ake yi tamkar wata babbar kasada, duk kuma da amincewa da shirin, da Majalisar dokoki ta Bundestag ta yi.