1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mr Musharraf na jiran hukuncin kotun koli

October 7, 2007
https://p.dw.com/p/Bu97

Manyan alkalan kotun kolin Pakistan na nazarin kundin tsarin mulkin kasar, don tantance sahihancin takarar shugaba Pervez Musharraf, a zaben shugaban kasa daya gudana a jiya.Hakan kuwa yazo ne, bayan ci gaba da tababar nasarar da Mr Musharraf din ya samu ne a zaben na shugaban kasa, a yayin da yake rike da ragamar rundunar sojin kasar.

Tuni dai Mr Musharraf ya magantu, don ganin cewa ba´ayi masa sakiyar da ba ruwa ba:

Mr Pavez Musharraf yace ko da akwai adawa ko akasin haka, dimokradiyya itace mulki na mafiya rinjayen jama´a, a don haka shine ya lashe wannan zabe, bayan samun kashi kusan 54 zuwa 55, na kuriun da yan majalisun dokokin kasar suka ka da:

Tuni dai hukumar zabe ta kasar tace, dole ne sai Mr Musharraf ya samu tubarrakin kotun kolin kasar, kafin ya tabbata cewa shine ya lashe wannan zabe na jiya asabar.