1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane da dama sun mutu a Somaliya

July 31, 2017

Jamia'ai a Somaliya sun ce mutane 25 ne suka salwantarsu bayan wata arangama tsakanin mayakan Al Shabaab da dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afirka ta AU.

https://p.dw.com/p/2hQ2x
Somalia kenianische Soldaten der Afrikanischen Union
Hoto: Getty Images/AFP/AU-UN Ist Photo/S. Price

Akalla mutane 25 ne jami'ai suka tabbatar da salwantarsu a Somaliya bayan wata arangama tsakanin mayakan Al Shabaab da dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afirka ta AU. Lamarin dai ya faru ne a yankin Shabelle kamar yadda hukumomin kasar suka tabbatar.

Mayakan Al Shabaab, sun yi ikirarin halaka dakarun na AU 39 a kwanton baunar da suka yi wa sojojin, sai dai har ya zuwa yanzu ba su tabbatar da sahihancin ikirarin ba. Rahotanni sun ce mayakan na tawaye na tsananta hare-hare kan dakarun na kasashen na Afirka.

Kimanin dakaru dubu 20 ne dai kungiyar ta AU ta girke a Somaliyar musamman saboda fuskantar 'yan jihadin na Al Shabaab.