1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Myanmar: MDD na son a gyara sansanoni

Abdul-raheem Hassan
January 24, 2018

MDD ta bukaci wannan dama ne domin inganta sansanonin da ta gina wa dubban musulman Rohingya da ke gudun hijira a kasashe makobta domin ba su kwarin gwiwar dawowa kasarsu.

https://p.dw.com/p/2rRjZ
Myanmar Aufbau Lager für Rückkehr Rohingya Flüchtlinge
Hoto: picture-alliance/AP/T. Zaw

Wata tawagar kasa da kasa da ta ziyarci wasu sansanonin da ke kusa da kan iyakar kasara Myanmar da Bangaledesh sun ce gidajen jama'a ba sa kan tsarin da dan adam zai yi rayuwa a ciki.

Gwamnatin Myanmar na ci gaba da jan kafa wajen tantance dubban 'yan kasar da ake shirin maido su gida daga kasashen da suke gudun hijira, amma MDD ta nun shakku kan ingancin tsaro kan rayuwar wadanda za a dawar.

Hukumomin kula da 'yan gudun hijira na MDD sun kiyasta sama da musulman Rohingya dubu 600 rikicin jihar Rakhine ya tilasta musu tserewa zuwa kasar Bangaledesh tun a watan Agustan shekarar 2017.