Najeriya: An halaka manoma 8 a jihar Benue
May 9, 2017Talla
Kwamishinan 'yan sandar jihar ta Benue Bashir Makama ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa fulanin makiyaya sun kashe mutanen ne a lokacin wani hari da suka kai a daren Litinin washe garin Talatar nan a wasu kauyuka biyu na manoma a yankin Logo na Gabashin jihar ta Benue. Kuma ya ce rikicin ya samu asali ne lokacin da mutanen kauyukan na manoma suka yi yinkurin hana wa makiyayen yin kiwon dabbobinsu a cikin gonakkinsu.
Jihar Benue dai ta yi kaurin suna wajen fadace-fadacen manoma da makiyaya inda ko a shekarar da ta gabata, an halaka daruruwan mutane tare da kone gidaje kimanin dubu a wani kazamin fadan da ya barke tskanin manoman da makiya ya a garin Agatu na cikin jihar.