1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Rikicin siyasa da canji sheka

Gazali Abdou Tasawa
December 28, 2017

Wutar rikicin shugabanci na dada ruruwa a manyan jam'iyyun siyasar Najeriya tare da haddasa canjin shekar wasu 'yan siyasar daga wannan jam'iyya zuwa waccan.

https://p.dw.com/p/2q2s3
Muhammadu Buhari und Atiku Abubakar
Hoto: Atiku Media Office

A Najeriya a daidai lokacin da ya kasa da shekara daya da rabi a gudanar da zabe, guguwar neman gabaci ta taso a cikin jam'iyyun siyasar kasar na APC mai mulki da PDP mai adawa. A yayin da a Kano rikicin cikin gida ya kaure a jam'iyya mai mulki ta APC tsakanin 'yan Kwankwasiya da 'yan Gandujiya, tsohon mataimakin shugaban Najeriya kuma jigo a jam'iyyar APC, Atiku Abubakar ya canza sheka zuwa jam'iyyar adawa ta PDP.