1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Rufe filin jirgin sama na Abuja

Lateefa Mustapha Ja'afar
March 9, 2017

Najeriya: Ra'ayoyi sun banbanta sakamakon karkatar da akalar jigilar jiragen sama daga filin jirgin sama na Abuja zuwa na jihar Kaduna.

https://p.dw.com/p/2YtT4
Gyaran filin jirgin sama na Abuja da mayar da jigilar jiragen zuwa Kaduna
Gyaran filin jirgin sama na Abuja da mayar da jigilar jiragen zuwa Kaduna

A Najeriya ra'ayoyi sun ban-banta dangane da batun yin gyara a filin sauka da tashin jiragen sama na Abuja, inda a yanzu haka aka rufe filin tare kuma da karkatar da akalar jiragen da ke hada-hada a cikinsa zuwa jihar Kaduna da ke makwabtaka, har nan da tsahon makwanni shida masu zuwa.