1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya ta lashe gasar cin kofin Afirka na mata

December 3, 2016

Najeriya ta doke Kamaru a wasan karshe na cin kofin Afirka na mata wanda kasar ta Kamaru ta dauki nauyi.

https://p.dw.com/p/2ThK1
Nigeria Fußball Logo Nigeria Football Federation NFF
Hoto: Franck Fife/AFP/Getty Images

Najeriya ta lashe gasar cin kofin kwallon kafa na Afirka na mata, bayan doke kasar Kamaru da ci daya mai ban haushi. 'Yan wasan Najeriya sun samu nasarar jefa kwallon ana kusan tashi daga wasan.

Wasan wanda ya gudana a birnin Yawunde fadar gwamnati Kamaru, Najeriya ta zira kwallo a raga a mintoti 84, saura mintoci shida kadai a tashi a wasan, abin da ya jefa magoya bayan Kamaru kimanin 40,000 da ke cikin filin wasan cikin bakin-ciki.