1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Yunkurin yaki da cin hanci tare da ICPC

August 2, 2017

A kokarin da ake na kawo karshen matsalar hancin a Tarrayar Najeriya da ke kwan gaba kwan baya, gwamnatin kasar ta aiwatar da garambawul tare da maye gurbin shugaban hukumar ICPC da ta jima ta na tangal-tangal.

https://p.dw.com/p/2hanp
Nigeria Geld Geldscheine Naira in Lagos
Saidar kudin NajeriyaHoto: Getty Images

Duk da cewar hukumar EFCC ta yi kaurin suna tare da buwaya a tsakanin sarakuna dama talakawa na kasar, ga 'yar uwarta ta ICPC dai  karatun na kusan kama da karatun kurma ga batun yaki da cin hancin na  Tarrayar Najeriya da yanzu haka yake kwan gaba kwan baya. Abun kuma da ya kai gwamnatin kasar sauke shugaba na hukumar ICPC Ekpo Nta, tare da maye gurinsa  da Farfesa Bolaji Awosanaye da ake saran zai sake farfado da hukumar tare da kara mata karfi.

A baya hukumar ICPC ba ta yi armashi ba

Nigeria Symbolbild Korruption
Yaki da cin hanci na fuskantar tarnaki a NajeriyaHoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

Tun kafin ga nadin dai dama farfesan na zaman sakatare na majalisar bada shawara ta gwamnatin kan yaki da hanci, kuma daya a cikin manyan jagororin fafutikar. Babban laifin ICPC a karkashin Ekpo Nta dai a fadar ministan shari'a kuma babban jaforan yakin hanci na kasar Abubakar Malami, shi ne na gaza hukunta ko kuda a hukumar da hankalinta ke a kan ma'aikatan gwamnatin kasar a halin yanzu.

Abun da ake jira ga sabon shugaban ICPC

Nigeria Symbolbild Korruption
'Yan sandan Najeriya masu yaki da cin hanciHoto: picture alliance/NurPhoto

A cikin kokari na gyaran fuska da nufin biyan bukata dai, gwamnatin Tarrayar Najeriya na fatan ganin wannan sabon sauyin zai taimaka wajen kara fadada yaki da cin hancin da ya zuwa yanzu yafi karkata ga masu siyasa da sauran masu rike da manyan mukamai na gwamnati. Ana dai kallon kokari na karfafa ICPC ka iya kaiwa ga kara fadin yakin da nufin tunkarar matsakaita da kanana na ma'aikatan kasar da ake zargi da sata amma kuma suke tsira da abun da suka sata sakamakon gaza cika aikin na hukumar ta ICPC.