1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya:Za a kara bayyana barayin kasar

February 23, 2017

Shaidu da dama sun ce a shirye suke su kara bayyana sunayen wadanda suka saci dukiyyar kasa a Najeriya ga hukumar EFCC.

https://p.dw.com/p/2Y9KD
Nigeria Plakate und Aufkleber gegen Korruption
Hoto: DW/K. Gänsler

Mahukuntan Najeriya sun ce suna samun tururuwar masu tsegumin kudaden sata a kasar bayan shirin tsegumi mai ladan da ke tashe cikin kasar a halin yanzu.Kama daga motocin alfarma ya zuwa ga makudai na kudade dai sannu a hankali Najeriyar na fuskantar sabon yanayi a cikin yakin hancin da a baya ya fuskanci turjiya.Ko a tsakiyar wannan mako dai gwamnatin kasar ta ayyana gano wasu tsabar kudade har Naira miliyan dubu takwas da dari hudu da aka boye a cikin wani asusun da babu mai shi a kasar.

Ko bayan nan kuma jami'an hukumar EFCC sun yi nasarar kwace wasu motocin alfarma a gidan tsohon shugaban hukumar fice da shigi har 17 a wani abin da ke zaman alamun sabon tsarin na aiki.Kwadayi na kudade a cikin halin kunci dai a fadar Dr Garba Umar kari da ke zaman wani mai sharhi kan hali na zamantakewar al'umma a kasar ya yi hasashen cewar karuwar masu tsegumta satar zai taimaka a samu barayin kasar da dama.