Nigeria: 'Yan mata 110 sun bace a Dapchi
February 25, 2018Talla
Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da bacewar yara 'yan mata 'yan makarantar sakadaren kimiyya dake Dapchi a jihar Yobe bayan harin da 'yan Boko Haram suka kai hari makarantar a ranar Litinin da ta gabata inda suka yi awon gaba da dalibai da dama
Ministan yada labaran kasar Lai Mohammed a cikin wata sanarwa da ya fitar yace a kididdigar da suka yi daga cikin yara 'yan makarantar su 906 an tantance yara 110 wadanda har yanzu ba'a gano su ba.
Tun da farko a jiya Asabar Iyayen yara 'yan makarantar sun baiyana sunaye 105 na 'ya'yansu mata wadanda suka ce har yanzu babu labarinsu, kusan mako guda bayan da 'yan Boko Haram suka kai hari makarantar.
Kawo yanzu dai babu tabbas a game da makomar yaran.