1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar ta mayar wa Amirka martani

October 13, 2017

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta mayar da martani kan zargin da wasu daga cikin shugabannin sojin Amirka a Nijar suka yi na cewa ba a rasa hadin bakin al'ummar kauyen Tongo-Tango na kan iyaka da Mali ba.

https://p.dw.com/p/2loM8
Symbolbild Soldaten Nigeria
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta mayar da martani kan zargin da wasu daga cikin shugabannin sojin Amirka a Nijar suka yi na cewa ba a rasa hadin bakin al'ummar kauyen Tongo-Tango na kan iyaka da Mali ba, a harin da wasu 'yan ta'adda suka kai wa ayarin sojojin Nijar da na Amirka a yankin a makon da ya gabata inda suka kashe sojoji takwas da suka hada da na Amirka guda hudu.

A wata hira da ya yi da tashar DW a wannan Juma'a, ministan cikin gida na jamhuriyar Nijar Malam Bazoum Mouhamed ya bayyana cewa suna da tabbacin cewa al'ummar yankin na kyamar wadannan 'yan ta'adda duk da ya ke ba za a rasa baragurbi a cikinsu ba.

Wasu kafofin yada labarai na kasar ta Amirka ne dai suka ruwaito labarin da ke cewa shugabannin rundunar sojin Amirka a Nijar ta zargi al'ummar kauyen na Tongo-Tongo da bai wa 'yan ta'addan bayanai ga kasancewar sojojin a yankin nasu.