1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: 'Yan kwadago na so a yi yajin aiki

Mahaman Kanta/ASApril 28, 2016

Kungiyoyin fararen hula da na kwadago sun bukaci jama'a da su shiga yajin aiki saboda yin karen tsaye da hukumomi ke yi wa tsarin dimokradiyya.

https://p.dw.com/p/1Iejk
Niger Präsident Mahamadou Issoufou
Hoto: F. Batiche/AFP/Getty Images

Shugabannin kungiyoyin fararen hula na da 'yan kwadago a Nijar sun nemi masu sana'a da su kauracewa wuraren sana'o'insu don nuna rashin jin dadinsu game da rashin aiwatar da dimokadiyya kamar yadda ya dace a kasar wanda gwamnatin Shugaba Issoufou Mouhammadou ke yi.

Wakilinmu na Yamai Mahamman Kanta ya ce kungiyoyin sun ambata hakan ne dazu a wani taron manema labarai da suka kira. To sai dai duk da wannan kira da 'yan kwadagon suka yi, 'yan kasuwa a babbar kasuwar da ke birnin Yamai na cigaba da kasuwancinsu.