1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

?oƙarin Eu na kawo ƙarshen rikicin Nukiliyar Iran

Ibrahim SaniNovember 22, 2007
https://p.dw.com/p/CQTh

Wakilin Iran game da tattaunawar Nukiliya, Mr Saeed Jalili ya ce a ƙarshen watannan ne yake sa ran tattaunawa da kantoman Ƙungiyyar Tarayyar Turai, Mr Javier Solana.Tattaunawar a cewar rahotanni za ta kasance irinta ta farko ne, a ƙoƙarin da ake na samo bakin zaren warware rikicin Nukiliyar ta Iran. Bayan tattaunawar, Javier Solana zai yiwa Majalisar Ɗinkin Duniya bayanin yadda tattaunawar ta kasance. Hakan a cewar bayanai ka iya taimakon Majalisar gane inda aka kwana, a game da aniyar Iran ɗin na mallakar makamin na Atom. Ba sau ɗaya ba sau biyu ba, Iran ta dage kan cewa shirin ta na inganta rayuwar ´ Yan ƙasar ne, saɓanin zargin da ake na cewa shirin ka iya zamowa barazana ga Duniya.