1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Palasdinu: Kungiyar PLO ta yi watsi da Isra'ila

Gazali Abdou Tasawa
January 16, 2018

A kasar Palasdinu kwamitin gudanarwa na kungiyar kwatar 'yancin kasar Palasdinu wato OLP ya dauki mataki dakatar da amincewa da kasantuwar Isra'ila a matsayin kasa.

https://p.dw.com/p/2qtnJ
Palästina Israel Konflikt Versammlung PLO in Ramallah Mahmoud Abbas
Hoto: picture-alliance/AP Images/M. Mohammed

A kasar Palasdinu kwamitin gudanarwa na kungiyar kwatar 'yancin lasar Palasdinu wato PLO ya dauki mataki dakatar da amincewa da kasantuwar kasar Isra'ila a matsayin kasa, matakin ke a matsayin babban tuballin da aka kafa shirin zaman lafiya tsakanin Isra'ila da Palasdinawan. 

Kwamitin gudanarwa na Kungiyar ta PLO ya kada kuri'ar dawowa daga matakin amincewa da Isra'ila a matsayin kasa bayan wani taron kwanamki biyu da ya gudanar a birnin Ramalla na yammacin kogin Jodan a karkashin jagorancin shugaban Palasdinawan Mahmud Abbas. Wannan mataki na kungiyar PLO na a matsayin martani ga matakin da shugaba Trump na Amirka ya dauka a ranar shida ga watan Disambar da ya gabata na bayyana birnin Kudus a matsayin babban birnin Isra'ila.