1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Paparoma ya fara ziyara a Afirka

Zainab Mohammed AbubakarNovember 25, 2015

Birnin Nairobin kasar Kenya dai ita ce a kafar farko da shugaban darikar roman katolikan ya fara yada zango, a rangadin da zai yi a kasashe uku na Afirka.

https://p.dw.com/p/1HCOE
Kenia Papstbesuch Firgur des Papstes in der Holy Family Basilica in Nairobi
Hoto: DW/D. Pelz

Da yammacin yau ne ake saran Paparoma Francais zai gana da shugaba Uhuru Kenyata na Kenya, kafin ya jagoranci sajadar da mutane sama da dubu 500 za su halarta a gobe Alhamis.

Bayan kwanaki biyu a Kenya, shugaban darikar katolika mai shekaru 78 da haihuwa, zai shige zuwa kasar Yuganda kafin Janhuriyar Afirka ta tsakiya. Ziyarar da ake saran zai kammala ranar Litinin.

A kwai kimanin mabiya darikara roman katolika miliyan 180 a fadin nahiyar Afirka. Ziyarar ta paparoma Francis dai, ita ce ta 11 irinsa a wajen fadarsa ta Vatikan dake birnin Rome, tun da ya hau wannan mukami a shekara ta 2013.