1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Paul Biya: Za mu murkushe masu neman ballewa

December 1, 2017

Gwamnatin kasar Kamaru, ta yi alkawarin shafe dukkanin masu fafutikar ballewa da ke yanki mai amfani da turancin Ingilishi, saboda abin da ya kira bazanar da suke wa tsaron kasar.

https://p.dw.com/p/2obzf
Kamerun Präsident Paul Biya Archivbild 30.01.2013
Hoto: Patrick Kovarik/AFP/Getty Images

Shugaba Paul Biya na kasar Kamaru, ya yi alkawarin shafe dukkanin masu fafutikar neman ballewa daga kasar, wato mutanen nan da ke yanki mai amfani da Turancin Ingilishi, saboda abin da ya kira bazanar da suke wa tsaron kasar. A wani jawabin da ya yi da yammacin Alhamis, Shugaba Biya ya kuma ce mafusatan sun kashe akalla sojoji hudu tare da wasu jami'an 'yan sanda biyu cikin wannan mako.

Cikin watanni biyun da suka gabata ne dai aka rasa wasu fararen hula da dama a kasar ta Kamaru, lokacin da gwamnatin kasar ta kife masu da'awar ballewar, da suka ce ana nuna masu wariya. Bangaren na Ingilishin, na zargin mayar da su saniyar ware daga bangaren kasar mai amfani da Faransanci da kasar ta fifita.