1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rabon mukamai a Sudan ta Kudu

Nura Datti Kankarofi/ASJanuary 7, 2016

An cimma yarjejeniyar kan raba madafun ikon a Sudan ta Kudu da nufin samar da zaman lafiya tsakanin gwamnati da 'yan adawa.

https://p.dw.com/p/1Ha1T
Bildkombo Südsudan Riek Machar und Salva Kiir
Hoto: Getty Images/Zacharias Abubeker/Ashraf Shazly/Montage

A ranar Alhamis din nan ce dai masu saka idanun suka fadi cewar ma'aikatun kudi da tsaro da shari'a da kuma yada labaru za'a za su kasance a hannun mutanen Shugaba Salva Kiir, yayin da jagoran 'yan adawa kuma tsohon mataimakin shugaban kasar Riek Machar zai cigaba da rike mukaminsa.

Har wa yau, mukaman da suka hada da ministocin man fetur da na cikin gida za su kasance a hannun mutanen Machar sannan tsofaffin fursunonin siyasa wanda ba su da nasaba da bangaren Shugaba Kiir ko kuma Machar za su rike mukamin ministan harkokin kasashen waje, yayin da sauran 'yan adawa da ba sa dauke da makamai za su ja ragamar tafiyar da harkokin majalisar zartarwa.