1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rahoton shekara na kungiyar ƙwadago ta ƙasa da ƙasa

June 6, 2006
https://p.dw.com/p/Buv8

Mutane 115,yan gwagwarmayar ƙwatar yanci ma´aikata, su ka rasa rayuka, a shekara ta 2005, a sassa daban-daban na dunia.

Wannan alƙalumma, sun hito daga rahoton da haɗɗaɗiyar ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa da ƙasa, wato CISL, ta bayyana yau, a cibiyar ta, da ke birnin Brussels, na ƙasar Belgium.

Rahoton ya ce, bana,an samu ɗan ci gaba, idan a ka kwanta da shekara ta 2004, inda mutane 145 su ka mutu sanadiyar gwagwarmayar ƙwatar haƙƙoƙin ma´aikata.

Daga sahun ƙasashe 137 da a ka gudanar da bincike, a gano cewar, a ƙasar Colombia ne, ayyukan neman yancin ma´aikata ke tattare da haɗarruruka, fiye da ko inna cikin dunia.

A jimilce, yan ƙungiya 1.600 su ka fuskaci barzana kissa a shekara da ta wuce, a ƙasar, a yayin da aka tsaida 9.000.

Kazalika, ƙasashe kamar su Zimbabwe, Chine, Salvador Iran, Cambodjia, Djibouti da Gwatemala, na daga sahun wuraren da ƙungiyoyin ƙwatar yancin ma´aikata ke fuskantar uƙuba, daga gwamnati inji rahoton.

Shugaban ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa da ƙasa, Guy Ryder, ya bayana matuƙar damuwa, a game da halin da mata ma´aikata, na ƙasar Colombia, ke gudanar da ayyukan yau da kullum cikin barazana.

Guy Ryder, ya suka da kakkausar halshe, ga magabatan ƙasashen Koweit, Oman, Qatar, saudi- Arabia, Lybia da Jordan, inda sam-sam ,babu damar girka ƙungiyoyin ƙwadago.