1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ranar ƙananan yara ta duniya

November 20, 2007

Yau shekaru 18 kenan da zartas da ƙudurin kare ´yancin yara a duniya

https://p.dw.com/p/CPan
Yara a SaliyoHoto: AP

A lokacin da ta ke da shekaru 17 an zubawa Hasina guba ta acid a fuska a ƙasar ta wato Bangladesh. Hakan ya faru ne bayan wata hatsaniya da ta yi da wani tsoho wanda ya ɗauki wannan mataki a kan ta, inda ya watsa mata gubar a fuska don ya ja kunnenta. Hasina zata ci-gaba da rayuwa da tabon da gubar ta bari har tsawon rayuwarta.

Hasina ta ce “A lokacin ina shirye shiryen halartar wani buki ne wanda da ni da ´yan´uwana muka daɗe muna begensa. Daddare lokacin da na ke barci bayan bukin sai na ji an zuba mun guba a fuska. Da farko ban san abin da ya faru ba. Na ji kamar ruwan zafi aka zuba min, amma sai na yi ta jin ƙuna na yi ta kara ina neman a ba ni ruwa amma ba a ba ni ba.”

Hasina wanda yanzu ta cika shekaru 20 ta samu taimako daga asusun taimakon yara na MƊD wato UNICEF. An yi mata aikin tiyata da yawa. A gun wani taro da asusun UNICEF ya shirya a birnin Berlin, a karon farko Hasina ta samu ƙwarin guiwar bayyana abin da ya farun. Mai kula da ´yancin ƙananan yara a Jamus Sabine Christiansen ta kaɗu da jin labarin Hasina. Ta ce abin takaici ne ganin yadda har yanzu ake cin zarafin ƙanana yara a duniya baki daya.

Alkalumman asusun UNICEF na nuni da cewa ana azabtar da miliyoyin yara ko yin lalata da su a duniya. Asusun ya ce ana bautar da yara kimanin miliyan 200 a duniya baki ɗaya yayin da a duk shekara masu fataucin bil Adama na sace yara miliyan daya da dubu 200. Hakan kuwa na faruwa ne duk da ƙkudurin kare ´yancin yara na MƊD wanda ƙasashen duniya suka sanyawa hannu.

Ko da yake matsalolin yara a Jamus ya banbanta to amma shugabar UNICEF a ƙasar Heide Simonis tsohuwar Firimiyar jihar Schleswig-Holstein ta yi suka da rashin daidata al´amura a kasashen masu arziki.

Simonis ta ce “Muna masu ra´ayin cewa a kasa kamar Jamus da ake da ƙarancin kananan yara, da zai fi kyau idan aka saka batun ´yancin yara a dokar kasa. Ana ina mai yin tuni da cewa Jamus ta sanya hannu kan ƙudurin MƊD na ba da kariya ga yara bisa wasu sharaddu. Muna kira da a dage sharuɗɗan. Majalisar dokoki ta sha yin magana a dangane da haka.”

Shi kuwa mai magana da yawon UNICEF Rudi Tarneden cewa ya yi an samu ingantuwa abubuwa da yawa sakamakon kudurin ´yancin yara na MDD.

Tarneden ya ce “Hakika ba a zayyana ci-gaban da ake samu a cikin wani kundi. To amma ƙudurin ya ba da gudunmawa alal misali a nan Jamus wajen bawa dukkan iyaye ´yancin renon yara bayan rabuwa. Wannan dai wani abu ne dake da alaka kai tsaye da ƙudurin.”

Har yanzu ba a aiwatar da abubuwa da dama dake cikin kudurin kare ´yancin yara na MƊD ba alal misali yiwa dukkan jariri rajistar haihuwa kamar yadda kudurin ya nema. Rashin yin wannan rajista kuwa na janyo bacewar yara fiye da miliyan 50 a kowace shekara a duniya baki ɗaya.