1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rasha da Iran sun fara tattaunawa a birnin Teheran akan takadamar nukiliya

January 7, 2006
https://p.dw.com/p/BvDP

Kasashen Rasha da Iran sun fara tattaunawa a birnin Teheran akan shawarar da gwamnatin Mosko ta gabatar don ba Iran izinin samar da sinadarin uranium a cikin Rasha. Kasashen yamma karkashin jagorancin Jamus da Faransa da Birtaniya sun yi kira ga Iran da ta amince da wannan tayi, to amma gwamnati a Teheran ta dage kan cewar ita ma zata iya sarrafa uranium din a cikin kasarta. Rasha dai na kokarin kawo karshen kace-nace da ake yi tsakanin Iran da Amirka, wadda ke zargin Iran din da shirin kera makaman nukiliya a boye. Shugaba Mahmud Ahmedi-Nejad ya ce kasarsa zata fara aikin binciken sarrafa karafan nukiliya duk da barazanar da KTT da Amirka suka yi na mika Iran din a gaban kwamitin sulhun MDD don kakaba mata takunkumi.