1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin zaman lafiya a Somalia na ci gaba da tsananta

May 18, 2006
https://p.dw.com/p/Buxr

Mutane a kalla biyar ne suka rugamu gidan gaskiya, wasu kuma da dama suka jikkata a can birnin Magadishu na kasar Somalia.

Hakan kuwa ya biyo bayan wani dauki ba dadi ne da akayi a tsakanin yan yakin sa kai na Islama da kuma madugan yaki na kasar.

Wannan arangama dai tazo ne a dai dai lokacin da daruruwan mutane suka gudanar da wata zanga zangar lumana na bukatar zaman lafiya a kasar.

A yan makonni kadan da suka gabata wannan arangama a tsakanin bangarorin biyu an kiyasta cewa tayi ajalin mutane kusan 150 a kasar.