1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari a birnin Maiduguri ya halaka mutane da dama

Yusuf BalaOctober 2, 2015

A cewar shelkwatar jami'an sojan kasar ta Najeriya da ke Abuja, mutane 14 ne suka rasu a cikin harin ciki kuwa har da 'yan bindigar.

https://p.dw.com/p/1Ghjf
Nigeria - Maiduguri
Mutane a wurin da aka kai farmakiHoto: picture-alliance/AP Photo/Jossy Ola

Sama da mutane 10 ne suka rasu yayin da wasu 39 suka samu raunika bayan da wasu 'yan kunar bakin wake hudu suka kai farmaki a birnin Maiduguiri fadar gwamnatin jihar Borno kamar yadda jami'an sojan Najeriyar suka bayyana a ranar Juma'an nan.

A cewar shelkwatar jami'an sojan kasar ta Najeriya da ke Abuja, mutane 14 ne suka rasu a cikin harin ciki kuwa har da 'yan bindigar sannan 39 suka samu raunika a harin na cikin daren Alhamis.

Sanarwar jami'an ta kara da cewa 'yan bindigar guda uku sun tashi jigidar bam da ke jikinsu yayin da guda dayan kuma ya tashi nasa bam din a gaban masallaci.

Tun bayan da mayakan na Boko Haram suke fiskantar barin wuta daga dakarun sojan kasar da na kasashe makwabtan Najeriya yanzu sun mike da kai hare-hare irin na sari ka noke da ke karewa mafi akasari kan fararen hula.