1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikici ya ɓarke a zirin Gaza

June 14, 2007
https://p.dw.com/p/BuIv

Shugaban hukumar Palestinawa Mahamud Abbas, ya kiri taron ƙoli, na hukumar zartaswa ta ƙungiyar fatah,da kuma PLO, domin tantana rikicin da ya turnuƙe, tsakanin Hamas da Fatah a zirin Gaza.

A tsukin sati 2 da su ka wuce, a ƙalla mutane 80 su ka rasa rayuka a cikin wannan rikici.

A yau alhamis, ƙarin wasu mutane 14, dukkan su na ɓangaren Fatah, su ka kwanta dama,a sanadiyar wannan tashe-tashen hankulla.

A halin da ake ciki, dakarun Hamas, sun bayyana kwace cibiyoyin tsaro na shugaban hukumar Palestinawa dake Gaza.

A yayin da ta ke huruci, a game da wannan abun al´ajabi, wakiliyar Palestinu a ƙungiyar tarayya Turai, Leila Shahid,ta ce nan gaba a yau , Mahamud Abbas, zai rushe gwamnatin haɗin kai da a aka girka tsakanin Fatah da Hamas.

A nasu ɓangare, ministocin harakokin waje na ƙasashen ƙungiyar musulmi ta dunia, OIC,sun bayyana adawa, ga matakin da Majalisar Ɗinkin Dunia ke shirin ɗauka, na tura dakarun shiga tsakani, a zirin Gaza.