1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin Ethiopia da Erythrea

April 25, 2007
https://p.dw.com/p/BuMp

Gwamnatin Adis Ababa, ta zargi Erythrea, da hannu a cikin harin da wasu mutane ɗauke da makamai, su ka abkwa wata tashar binciken man petur, da ke ƙasar Ethiopia ranar jiya talata.

A cikin wata sanarwa da ministan watsa kabarai na kasar Ethipia ta karanata ya ce ƙungiyar tawayen ONLF da ta daujki alhakinkai wannanhari a da alakarat kut da kut da fadar mulkinAsmara.

Babu shakka a cewar ministan Erythera ce, ta kitsa wannan hari da farko har ƙarshen sa, tare da haɗin gwiwar yan tawayen ONLF.

A saƙon yanar gizo da ta aika, wannan ƙungiyar tawaye da ke neman yancin yankin Ogaden na Ehtiopia, ta ce zata ci gaba da kai hare-hare, har sai ta cimma burin ta.

A nata ɓangare, Erythrea tunni ! ta maida martani, ga zargin na Ethiopia.

Kakakin gwamnatin ƙasar Ali Abdu,ya ce wannan zargi ba shi da tushe bare makama.